Tarihin imam Ali (A.S)

AMIRUL MIMINA IMAM ALI (A.S.)

Lakabinsa: Amirul munin, Sayyidul muslimin, Imamul muttakin, Ka’idul gurril muhajjalin, sayyidul ausiya, sayyidul arab, Almurtada, Ya’asubuddini, Haidar, Al-anza’al badin, Asadul-Lah.

Alkunyarsa: Abul Hasan, Abul Hasanain, Abul Sibtain, Abu Raihanatain, Abu Turab.

Mahaifinsa: Abu Talib (Baffan Annabi) Imran ko kuma Abdu manaf dan  Abdul Mutallib.

Mahaifiyarsa: Fatima Bintu Asad.

Ranar Haihuwarsa: Ranar Juma' a 13 ga Rajab.

Gurin  Haihuwarsa: Cikin Ka'aba Dakin Allah mai  alfarma.

Shekarar Haihuwarsa: Shekara talatin bayan Shekarar Giwaye.

Adadin ‘ya’yansa: masu tarihi sun yi sabani kan yawan ‘ya’yansa amma suna tsakanin 25 ne zuwa 33 a ruwayoyin daban daban. Wasu na cewa, `ya'yansa: 36, 18 da cikinsu maza ne 18 kuma mata, Mazan su ne:

1) Al- Hasan Mujtaba

2) Husain

3) Muhammad Bin Hanafiyya

4) Abbas Akbar wanda ake yi wa alkunya da Abul Fadli

5) Abdullahil Akbar

6) Ja'afarul Akbar

7) Usmanul Akbar

8) Muhammad Asgar

9)Abdullahil Asgar

10)Abdullah wanda ake yi wa Alkunya da Abu Ali.

11) Aun

12) Yahya

 13) Muhammadul Awsat

 14) Usmanul Asgar

15) Abbasul Asgar

16) Ja'afarul Asgar

17) Umarul Akbar

18) Umarul Asgar

Mata kuwa su ne:

1 ) Zainabul Kubra,

2) Zainabul Sugra wadda ake kira Ummu Kulsum,

3) Ramlatal Kubra

4) Ummul Hasan

5) Nafisatu

6)Rukayyatus Sugra

7) Ramlatul Kubra

8) Rukayyatul Kubra

9) Maimunatu

10) Zainabus Sugra

11 ) Ummu Hani

12) Fatimatus Sugra

13) Imamatu

14) Khadijatus Sugra

15) Ummu Kulsum

16) Ummu Salama

17) Hamamata

18) Ummu Kiram

Matansa:

1-Fadimatuz-Zahra’yar manzon Allah (A.S)

2- Amama ‘yar Abil Asi

3-Ummul banin Alkilabiyya

4-Laila ‘yar Mas’ud

5-Asma’u ‘yar Amis 

6-Assahba’u ‘yar Rabi’a (ummu Habib)

7-Khaula ‘yar Ja’afar 

8-Ummu Sa’ad ‘yar Urwa

9-Makhba’a ‘yar Imru’ul kais.

Hatiminsa: Almulku Lillahi Wahidul Kahhar (Mulki na Allah ne Shi kadai mai cikakken rinjaye).

Haihuwar Imam Ali (A.S): Imam Ali (A.S) shi ne na farko cikin jerin imaman gidan Annabta kuma shi ne wasiyyin manzon Allah (S.A.W). An haife shi ne a cikin dakin Allah mai alfarma watau ka'abah a daidai ranar 13 ga watan Rajab shekara ta 23 kafin hijira. Yanzu haka dai kabarinsa yana Najaf dake kasar Iraki.

Yakokinsa: ya yi musharaka a yakokin manzo (S.A.W) gaba daya banda yakin Tabuka da manzo ya umarce shi da ya zauna a Madina domin tafiyar da al’amuranta amma yakokin da ya jagoranta da kansa a lokacin halifancinsa su ne: Aljamal da Siffaini da Annahrawan.

Dalilin Rasuwarsa: Ibn Muljam ne ya kashe shi sakamakon harin ba zata da ya kai masa yana salla a cikin masallacin Kufa.

Tsawon rayuwarsa: shekar 63.

Tsayin imamancinsa: shekara 30.

Tarihin shahadarsa: Daren jumma’a 21 ga watan azumi 40H.

Wurin da ya yi shahada: Masallacin Kufa.

Dalilin shahadarsa: Saran takobin nan na la’ananne Abdurrahman dan maljam yana mai  sujada a mihrabin masallacin kufa.

Inda aka binne shi: Yankin nan na gariyyi a garin Najaf madaukaki.

Hafiz Muhammad Sa’id Kano Nigeria
Hfazah@yahoo.com