HUDUBA TA BIYAR

[Daga maganarsa yayin da aka karbi ran manzon Allah (S.A.W) Abbas da Abu Sufyanu suka yi masa Magana akan su yi masa bai�a kan halifanci, wannan kuma ya faru ne bayan an riga an gama yi wa Abubakar bai�a a Sakifa, a cikin Hudubar yana mai hani ga fitina, yana kuma bayyana dabi�arsa da iliminsa]

[Hani Ga Fitina]

Ya ku mutane! Ku keta ta cikin ambaliyar fitina da jirgin tsira, ko karkata ga barin hanyoyin k�iyayya, ko sanya hulunan alfahari. Wanda duk ya tashi sama da fukafuki ya rabauta, ko kuma ya mika wuya sai ya hutar, ruwa ne mai jirkita,[1] kuma lomace da take shake mai hadiyarta, kuma mai debe �ya�yan itaciya ba a lokacin nunarta ba kamar mai shuka ne ba a kasarsa (gonarsa) ba.

�[D�abi�arsa Da Iliminsa]

Idan na yi magana sai su ce: Ya yi kwad�ayin mulki, idan na yi shiru sai su ce ya ji tsoron mutuwa! A�aha wallahi! Sam ba haka ba ne! bayan faruwar �yar waccan[2] da waccan d�ayar[3]!, wallahi! D�an Abi d�alib ya fi nutsuwa da mutuwa fiye da nutsuwar jariri da nonon babarsa, a�aha! tabbas kad�ai ya tattare a cikin b�oyayyen ilimin da, da na bayyanar da shi da kun d�imauce kun raurawa irin raurawar igiya a cikin rijiya mai zurfi.

Hafiz Muhammad Sa�id Kano Nigeria
[email protected]

[1] - Halifanci da al�amuran tafiyar da sha�anin mulki da al�umma.

[2] - �Yar waccan: fadinsu cewa ya yi kawadayin mulki.

[3] - 34- waccan dayar: fadinsu ya ji tsoron mutuwa.